Gwamnan jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje ya umarci wasu hakimai dake jihar da kada su halarci bikin Hawan Daushe da Sarkin Kano, Muhammad Sunusi II zai gudanar.
A cikin wata sanarwa,Abba Anwar mai magana da yawunsa ya fitar, Ganduje ya yi kira ga hakiman da su yi murnar bikin sallah a masarautunsu.
Wani sako dake ya wo a kafafen sadarwa na nuni da cewa hakiman da basa karkashin masarautar Kano za su zo a yi bikin Hawan Daushe da su karkashin masarautar Kano.
“Akan wasu kiraye-kiraye dake yawo a kafafen sadarawar zamani dake cewa dukkanin hakimai su halarci Hawan Daushe a fadar mai martaba sarkin Kano. Gwamnatin Kano na umartar dukkanin Hakimai su halarci hawan Daushe karkashin masarautunsu,” a cewar sanarwar.
Sanarwar ta kara da cewa hakiman za su gudanar da dukkanin bukukuwan a karkashin sarakunan su masu daraja ta daya.