Ganduje ya hana Hakimai zuwa Hawan Daushe

Gwamnan jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje ya umarci wasu hakimai dake jihar da kada su halarci bikin Hawan Daushe da Sarkin Kano, Muhammad Sunusi II zai gudanar.

A cikin wata sanarwa,Abba Anwar mai magana da yawunsa ya fitar, Ganduje ya yi kira ga hakiman da su yi murnar bikin sallah a masarautunsu.

Wani sako dake ya wo a kafafen sadarwa na nuni da cewa hakiman da basa karkashin masarautar Kano za su zo a yi bikin Hawan Daushe da su karkashin masarautar Kano.

“Akan wasu kiraye-kiraye dake yawo a kafafen sadarawar zamani dake cewa dukkanin hakimai su halarci Hawan Daushe a fadar mai martaba sarkin Kano. Gwamnatin Kano na umartar dukkanin Hakimai su halarci hawan Daushe karkashin masarautunsu,” a cewar sanarwar.

Sanarwar ta kara da cewa hakiman za su gudanar da dukkanin bukukuwan a karkashin sarakunan su masu daraja ta daya.

More News

Yadda rikici a kan gishirin N20 ya yi sanadiyyar mutuwar wani mutum a Kano

Wani magidanci mai suna Zakari Hamza mai shekaru 45, ya gamu da ajalinsa a hannun kanen matarsa, wani Magaji Salisu saboda gishirin N20. Dan marigayin,...

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan IPOB 5

Dakarun rundunar sojan Najeriya da kuma ta rundunar sojan ruwan Najeriya a ranar Talata sun kashe mayaƙan ƙungiyar IPOB guda biyar a yayin musayar...

ĆŠan agajin Izala ya samu lambar yabo, kujerar hajji, kyautar mota bayan ya tsinci naira miliyan 100 ya mayar wa mai su

Salihu AbdulHadi Kankia, mamba ne na kungiyar agaji ta kungiyar Jama’atu Izalatil Bid’ah Wa Iqamatus Sunnah (JIBWIS), ya samu yabo da tukuicin mayar da...

Musulmi a Zaria sun yi taron addu’o’i saboda mummunan halin matsi da Najeriya ke ciki

Musulmi a garin Zaria na jihar Kaduna, sun gudanar da addu'a ta musamman domin neman taimakon Allah kan halin da 'yan Najeriya ke ciki...