Abdullahi Umar Ganduje, Gwamnan Kano, ya raba wa ‘yan bautar kasa guda 6 da ‘yan fashi su ka kaiwa hari, N600,000.
Gwamnan wanda ya bada kyautar a ranar juma’a 29 ga watan Maris, ya ce ya ba da kudin ne saboda ya kwantarwa da wadanda abin ya shafa hankali. Sannan Gandujen ya roki ‘yan bautar kasar da su zamanto mutane na gari, wadanda al’ummar baya da kasa zata yi alfahari da su.
Ganduje ya rabawa ‘yan bautar kasa dubu dari – dari
Sannan ya yiwa ‘yan bautar kasar alkawarin ba su tsaro yadda ya kamata a fadin jihar Kano, sannan ya yi musu alkawarin zai cigaba da basu alawus na N5,000 da ya saba basu duk karshen wata.
Sannan ya kara da cewa, ma’aikatan fannin lafiya, za a ba su alawus fiye da na kowa.
Ba dadewa, mu ka samu rahoton cewa ‘yan fashi sun kaiwa wasu masu bautar kasa su 6 hari, akan hanyar Gwarzo zuwa Karaye.