Everton ta lallasa Man United

Premier

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Manchester United ta debi kashinta a hannu bayan Everton lallasa ta 4-0 a wasan mako na 35 a Premier da suka fafata ranar Lahadi a Goodison Park.

Everton ta ci kwallo biyu tun kan aje hutun rabin lokaci ta hannun Richarlison de Andrade da kuma Idrissa Gueye.

Bayan da suka koma zagaye na biyu aka kara zura kwallo biyu a ragar United ta hannun Lucas Digne da kuma Theo Walcott.

United, wadda ta buga karawar kamar ‘yan wasanta ba su da lafiya ta samu dama daya kacal da ta buga kwallo ta nufi raga saura minti hutu a tashi daga fafatawar.

Marcus Rashford ne ya samu damar a cikin masu tsaron bayan Evrton, ya kuma buga kwallo ta wuce saman kan mai tsaron raga Jordan Pickford.

Wannan nasarar ta kai Everton zuwa mataki na bakwai a teburin Premier, hakan zai iya kai ta gasar Europa a badi, ita kuwa United ta ci gaba da zama a matakinta na shida.

Sauran maki biyu ne tsakanin United da Arsenal ta biyar a teburi, wadda za ta fafata da Crystal Palace ranar Lahadi.

A ranar Talata ne Barcelona ta fitar da Manchester United daga gasar cin kofin Zakarun Turai ta bana, kuma ba ta kai bantenta a FA Cup ba, kuma Manchester City ce ta lashe Caraboa Cup na shekarar nan.

Everton ta taba cin United 3-0 a gasar Premier ranar Lahadi 26 ga watan Afirilun 2015 a Goodison Park.

Yadda kungiyoyin suka murza-leda.

Hakkin mallakar hoto
BBC Sport

More News

EFCC na neman Yahaya Bello ruwa a jallo

Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (Economic and Financial Crimes Commission) ta bayyana tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello a matsayin...

Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a...

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon ĆŠaya Daga Cikin Ćłan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon É—aya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...