Everton ta lallasa Man United

Premier

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Manchester United ta debi kashinta a hannu bayan Everton lallasa ta 4-0 a wasan mako na 35 a Premier da suka fafata ranar Lahadi a Goodison Park.

Everton ta ci kwallo biyu tun kan aje hutun rabin lokaci ta hannun Richarlison de Andrade da kuma Idrissa Gueye.

Bayan da suka koma zagaye na biyu aka kara zura kwallo biyu a ragar United ta hannun Lucas Digne da kuma Theo Walcott.

United, wadda ta buga karawar kamar ‘yan wasanta ba su da lafiya ta samu dama daya kacal da ta buga kwallo ta nufi raga saura minti hutu a tashi daga fafatawar.

Marcus Rashford ne ya samu damar a cikin masu tsaron bayan Evrton, ya kuma buga kwallo ta wuce saman kan mai tsaron raga Jordan Pickford.

Wannan nasarar ta kai Everton zuwa mataki na bakwai a teburin Premier, hakan zai iya kai ta gasar Europa a badi, ita kuwa United ta ci gaba da zama a matakinta na shida.

Sauran maki biyu ne tsakanin United da Arsenal ta biyar a teburi, wadda za ta fafata da Crystal Palace ranar Lahadi.

A ranar Talata ne Barcelona ta fitar da Manchester United daga gasar cin kofin Zakarun Turai ta bana, kuma ba ta kai bantenta a FA Cup ba, kuma Manchester City ce ta lashe Caraboa Cup na shekarar nan.

Everton ta taba cin United 3-0 a gasar Premier ranar Lahadi 26 ga watan Afirilun 2015 a Goodison Park.

Yadda kungiyoyin suka murza-leda.

Hakkin mallakar hoto
BBC Sport

More News

APC ta dakatar da Ganduje a matakin gunduma

Mambobin jam'iyyar APC a mazabar da ke Karamar Hukumar Dawakin Tofa a Jihar Kano sun dakatar da Shugaban Jam’iyyar APC na kasa Abdullahi Ganduje. ...

Wani mutumi ya kashe mahaifiyarsa a kan kudi

Jami’an rundunar ‘yan sandan jihar Osun sun kama wani mazaunin kauyen Kajola da ke kusa da Apomu a jihar mai suna Lukman Adejoju bisa...

Mayaƙan Boko Haram Biyu Sun Miƙa Kansu Ga Sojoji

Rundunar dakarun soja ta ƙasa da ƙasa wato Multi National Task Force(MNJTF) a turance shiya ta 3 dake Monguno a Najeriya ta bayar da...

Sojoji a birnin Ibadan  sun kama Æ´an fafutukar kafa Æ™asar Oduduwa

Dakarun rundunar sojan Najeriya  sun samu nasarar kama wasu mutane masu fafutukar kafa ƙasar Oduduwa a birnin Ibadan na jihar Oyo. Masu fafutukar sanye da...