EFCC ta kama mota makare da kudi a Sokoto

Mahmoud Yakubu

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Gabanin zaben gwamnoni da na ‘yan majalisar jihohi, an kama wata mota makare da kudi a jihar Sokoto.

Hukumar yaki da cin hanci da zagon kasa ta EFCC tare da jami’an tsaro ne suka kama mota kirar Jeep makare da kudi da ake zargin za a yi amfani da su ne wajen sayen kuri’u a jihar Sokoto.

An kama motar mai lamba ABC 924 LU a kan titin Garba Duba da ke Sokoto a daren Juma’a da karfe 10:30 inda aka kai motar hedikwatar ‘yan sanda a jihar Sokoto.

Daga nan ne aka fito da buhunhunan kudi domin yin bincike.

An yi ta kokarin jin ta bakin kakakin ‘yan sanda kan lamarin, yayin da jami’an tsaron suka hana daukar hotunan kudin.

Sai dai ana sa rai hukumar ‘yan sanda za ta yi taron manema labarai a yau Asabar kan lamarin.

‘Yan kwanaki kafin zaben shugaban kasa ne wani hoton bidiyo ya bayyana a shafukan sada zumunta na wani jirgin sama makare da kudi a wani filin jirgin.

Hakan kuma ya jawo ce-ce-ku-ce, inda wasu ‘yan Najeriya suka rika ganin cewa kudin sayen kuri’u ne.

Haka kuma, an samu rahotannin sayen kuri’u a wasu jihohi inda aka rika raba kudi, da silifas da maganin sauro da wasu kayan masarufi.

Irin wannan rabon kudi da kayyyaki a lokacin zabe dai abu ne da INEC ta haramta, sai dai duk da haka a kan sami wuraren da ake yi.

More News

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miÆ™ata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaÆ™i da yiwa tattalin arzikin Æ™asa ne ya hana shi bayyana...

Ƴan sanda sun kama mutane biyu dake samarwa ƴan fashin daji makamai a jihar Kaduna

Rundunar Æ´an sandan jihar Kaduna ta ce tana tsare da wasu mutane biyu da ake zargi da safarar bindiga a jihar. A wata sanarwa ranar...