Dan Hakika Zai Yadda Wani Yayi Jima’i Da Matarsa – Rahoton BBC

[ad_1]








Neman matan juna ga mabiya kungiyar Hakika ba laifi ba ne, wata sabuwar akida da ta bulla a arewacin Najeriya. Cikakkun ‘yan Hakika za su iya neman matan juna da kuma barin yin sallah da azumi, kamar yadda wani dan kungiyar ya shaida wa BBC.

Ya ce idan dan hakika ya kai kololuwar akidar zai iya yarda wani da ya kai matsayinsa ya nemi matarsa. “Idan na kai matakin, shi ma ya kai matakin zai iya nema ba wani abu ba ne a Hakika.”

A cewarsa, ba haka kawai suke barin sallah ko azumi ko kuma tarawa da mata ba, sai an bi wani mataki da ke ba wa mabiyi damar yin hakan, matakin da suke kira Tarbiyatul Askaru.

Ya ce “duk mutumin da aka ce ya yi Tarbiyatul Askaru zai fahimci kan sa, ya san wane ne Allah. Kuma idan ka yi nisa za ka shafe komai, ka daina ganin laifin komai,”yana jaddada cewa isa wannan matakin yana samar da sauki wajen aikata ibada, kasancewar yin wadannan shika-shikan addinin Musuluncin ba wajibi ba ne.




[ad_2]

More News

EFCC na neman Yahaya Bello ruwa a jallo

Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (Economic and Financial Crimes Commission) ta bayyana tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello a matsayin...

Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a...

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon Ɗaya Daga Cikin Ƴan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon ɗaya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...