Mutane da yawa sun samu raunuka kuma ana tunanin daya ya mutu a harbin da aka yi da misalin karfe goma da minti arba’in da biyar agogon kasar wato karfe tara da minti arba’in da biyar kenan agogon a kusa da titin Oktoberplein.
‘Yan sanda sun ce dan bindigar ya tsere. An dakatar da ayyukan jiragen kasa kuma an umarci makarantu da su rufe kofofinsu.
‘Yan Sandan da ke yaki da ta’addanci sun bayyana cewa “harin ta’addanci ne”.
Firayim ministan kasar Mark Rutte ya ce ya shiga matsananciyar damuwa kuma ya soke zaman tattaunawarsa da sauran jami’an gwamnati na mako-mako.
Rahotanni sun bayyana cewa jami’an tsaro sun umarci babban asibitin koyarwa na Utrecht da ya bude dukkan dakunan bayar da taimakon gaggawa don kula da wadanda suka samu raunuka.
Wani ganau ya bayyana wa manema labarai cewa “wani mutum ne ya fara harbi ta ko’ina”.
Wani kuma ya bayyana cewa ya ga wata mace da jini a hannuwanta da kayanta.
“Na sanya ta a cikin motata na taimake ta,” ya ce. “Lokacin da ‘yan sanda suka iso wurin, ba ta cikin hayyacinta.”
Babu tabbas kan yawan mutanen da suka yi rauni ko kuma girman raunukan da suka samu.
[ad_2]