Dan bindiga ya bude wuta a jirgin kasa

Shooting in Utrecht 18 March 2019

‘Yan sanda masu yaki da ta’addanci a wurin da aka kai harin

Wani dan bindiga ya bude wuta a cikin wani jirgin kasa a birnin Utretch da ke kasar Netherlands

Mutane da yawa sun samu raunuka kuma ana tunanin daya ya mutu a harbin da aka yi da misalin karfe goma da minti arba’in da biyar agogon kasar wato karfe tara da minti arba’in da biyar kenan agogon a kusa da titin Oktoberplein.

‘Yan sanda sun ce dan bindigar ya tsere. An dakatar da ayyukan jiragen kasa kuma an umarci makarantu da su rufe kofofinsu.

‘Yan Sandan da ke yaki da ta’addanci sun bayyana cewa “harin ta’addanci ne”.

Firayim ministan kasar Mark Rutte ya ce ya shiga matsananciyar damuwa kuma ya soke zaman tattaunawarsa da sauran jami’an gwamnati na mako-mako.

Rahotanni sun bayyana cewa jami’an tsaro sun umarci babban asibitin koyarwa na Utrecht da ya bude dukkan dakunan bayar da taimakon gaggawa don kula da wadanda suka samu raunuka.

Wani ganau ya bayyana wa manema labarai cewa “wani mutum ne ya fara harbi ta ko’ina”.

Wani kuma ya bayyana cewa ya ga wata mace da jini a hannuwanta da kayanta.

“Na sanya ta a cikin motata na taimake ta,” ya ce. “Lokacin da ‘yan sanda suka iso wurin, ba ta cikin hayyacinta.”

Babu tabbas kan yawan mutanen da suka yi rauni ko kuma girman raunukan da suka samu.

[ad_2]

More News

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miÆ™ata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaÆ™i da yiwa tattalin arzikin Æ™asa ne ya hana shi bayyana...

Ƴan sanda sun kama mutane biyu dake samarwa ƴan fashin daji makamai a jihar Kaduna

Rundunar Æ´an sandan jihar Kaduna ta ce tana tsare da wasu mutane biyu da ake zargi da safarar bindiga a jihar. A wata sanarwa ranar...