Ana tunanin ta gudo ne daga Gandun Namun Daji na Kaziranga inda dabbobi 92 suka mutu a ‘yan kwanakin nan saboda ambaliyar ruwa.
Jami’an wata kungiyar masu fafutukar kare hakkin namun dawa sun isa gidan kuma sun samar wa damisar hanyar fita zuwa daji.
A cewar Gidauniyar Namun Dawa ta Indiya WTI, an fara ganin damisar ne kusa da wani babban titi ranar Alhamis.
Gidauniyar ta ce babu mamaki, kaiwa da komawar da ake yi a kan titin ya matsa mata don haka ta nemi wannan gidan ta shiga, wanda kuma a kusa da babban titin yake.
“Ta yi matukar gajiya kuma ta samu bacci mai kyau,” a cewarsa.
Sai dai Migidan, Motilal, ya tattara kan iyalinsa kaf a lokacin da ya ga shigowar damisar.
“Abin sha’awa shi ne babu wanda ya matsa mata don ta samu hutawa sosai. Muna matukar girmama namun dawa a wannan yankin,” in ji Mista Barman.
“Molitilal ya ce zai adana zanin gadon da matashin kan da damisar ta hau ta kwanta.”
Jami’an WTI sun tsayar da motoci a kan babban titin tsawon awa guda sannan aka tayar da dabbar daga bacci. Ta tashi sannan ta bar gidan da misalin karfe biyar da rabi na yamma, ta tsallaka titin sannan ta bi hanyar dajin.
Gandun Namun Daji na Kaziranga na ajiye Damisa 110 amma babu ko daya da ya mutu a ambaliyar ruwan.
Dabbobin da suka mutu a dandun sun hada da barewa 54 da dorinar ruwa 7 da aladen dawa 6 da giwa daya.
Ambaliyar ruwa ta daidaita jihohin gabashin kasar na Bihar da Assam, inda ta kashe sama da mutane 100 da raba miliyoyin mutane da muhallansu.
Lokacin ruwa, wanda ke farawa daga watan Yuni zuwa watan Satumba ya jefa Nepal da Bangladesh cikin rudani.