Damisa ta kwanta baccin rana a kan gadon wani magidanci a Indiya

A tiger lying on a bed in Assam state

Damisar ta hau kan gado ta kwanta a cikin wani gida dake jihar Assam

An gano wata macen damisa wacce ta tsere daga wani gandun namun daji a jihar Assam da ambaliyar ruwa ta daidaita a Indiya, kwance a kan gadon wasu mazauna jihar.

Ana tunanin ta gudo ne daga Gandun Namun Daji na Kaziranga inda dabbobi 92 suka mutu a ‘yan kwanakin nan saboda ambaliyar ruwa.

Jami’an wata kungiyar masu fafutukar kare hakkin namun dawa sun isa gidan kuma sun samar wa damisar hanyar fita zuwa daji.

A cewar Gidauniyar Namun Dawa ta Indiya WTI, an fara ganin damisar ne kusa da wani babban titi ranar Alhamis.

Gidauniyar ta ce babu mamaki, kaiwa da komawar da ake yi a kan titin ya matsa mata don haka ta nemi wannan gidan ta shiga, wanda kuma a kusa da babban titin yake.


Mai gidan ya tsere a lokacin da ya tsinkayi damisar

Rathin Barman wanda ya jagoranci cire damisar daga gidan ya ce ta shiga gidan ne da misalin karfe 7 da rabi sannan ta kwanta ta yi ta bacci gaba daya ranar.

“Ta yi matukar gajiya kuma ta samu bacci mai kyau,” a cewarsa.

Sai dai Migidan, Motilal, ya tattara kan iyalinsa kaf a lokacin da ya ga shigowar damisar.

“Abin sha’awa shi ne babu wanda ya matsa mata don ta samu hutawa sosai. Muna matukar girmama namun dawa a wannan yankin,” in ji Mista Barman.

“Molitilal ya ce zai adana zanin gadon da matashin kan da damisar ta hau ta kwanta.”

Jami’an WTI sun tsayar da motoci a kan babban titin tsawon awa guda sannan aka tayar da dabbar daga bacci. Ta tashi sannan ta bar gidan da misalin karfe biyar da rabi na yamma, ta tsallaka titin sannan ta bi hanyar dajin.

Mista Barman ya ce babau tabbacin cewa ta shiga dajin ko kuma da shiga wani wajen ne dake kusa da dajin.

Gandun Namun Daji na Kaziranga na ajiye Damisa 110 amma babu ko daya da ya mutu a ambaliyar ruwan.

Dabbobin da suka mutu a dandun sun hada da barewa 54 da dorinar ruwa 7 da aladen dawa 6 da giwa daya.

Ambaliyar ruwa ta daidaita jihohin gabashin kasar na Bihar da Assam, inda ta kashe sama da mutane 100 da raba miliyoyin mutane da muhallansu.

Lokacin ruwa, wanda ke farawa daga watan Yuni zuwa watan Satumba ya jefa Nepal da Bangladesh cikin rudani.

More News

EFCC na neman Yahaya Bello ruwa a jallo

Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (Economic and Financial Crimes Commission) ta bayyana tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello a matsayin...

Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a...

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon ĆŠaya Daga Cikin Ćłan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon É—aya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...