Dalilin Da Ya Sa Saudiyya Ta Rage Adadin Mahajjatan Najeriya

[ad_1]

A bana maniyata 50,000 ne za su yi aikin Hajjin bana, sabanin dubu chasa’in da biyar, kuma tuni har an riga an kwashe alhazai dubu goma sha daya da dari hudu, wadanda a bana suna sauka a birnin Madina ne kai tsaye.

Shugaban hukumar Alhazai na kasa, Barr. Abdullahi Muktahar, ya ce rage yawan alhazan da aka yi, ya biyo bayan wani matakin aiki ne da hukumomin Saudiyya suka gindaya.

Daga cikin ka’idojin da suka gindaya, hukumomin na Saudiyya sun ce sun dauki wannan mataki ne domin sanin yawan bakin da za su je kasar don yi musu tanadi.

Sai dai kuma a Najeriya, bayanai sun nuna cewa sai makonnin biyun karshe da za a rufe filin jirgin sama ne wasu mutane ke biyan kudinsu na zuwa Makka.

Barr. Abdullahi ya yi kira ga masu kula da ayyukan hajji da masu ruwa da tsaki, da cewa ka da su bari masu suka su karkatar da hankalinsu.

Ya kara da cewa bin ka’idoji da dokokin da aka gindaya, musamman don gudanar da ayyuka cikin nasara, na da matukar muhimmanci.

Domin karin bayani saurari rahotan Medina Dauda:

[ad_2]

More News

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miÆ™ata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaÆ™i da yiwa tattalin arzikin Æ™asa ne ya hana shi bayyana...

Ƴan sanda sun kama mutane biyu dake samarwa ƴan fashin daji makamai a jihar Kaduna

Rundunar Æ´an sandan jihar Kaduna ta ce tana tsare da wasu mutane biyu da ake zargi da safarar bindiga a jihar. A wata sanarwa ranar...