Fatan Manchester City na lashe kofi hudu a bana na kara tabbata, bayan da ta samu nasara a wasan dab da na kusa da na karshe da ta kara da Brighton ranar Asabar a filin wasa na Wembley.
Kungiyar ta samu nasara ne da ci daya mai ban haushi, ta hannun Gabriel Jesus wanda ya daga ragar Brighton a minti na hudu da take wasa.
A yanzu dai kungiyar wadda ita ce ta lashe kofin Premier League na bara, tana ta biyu a kan teburin Premier da tazarar maki biyu tsakaninta da Liverpool wacce ke mataki na daya, inda kuma take da kwantan wasa daya.
Tuni dai kungiyar ta Etihad ta lashe kofin Caraboa na bana, bayan da ta yi nasara a kan Chelsea a bugun finariti.