Chiroki bai tallafa wa kowa a Kannywood ba – Ali Nuhu

Ali Nuhu

Hakkin mallakar hoto
Instagram/@realalinuhu

Image caption
Jigo a fina-finan Kannywood, Ali Nuhu, ya kalubalanci wani mai amfani da shafin Twitter cewa ya fada masa mutanen da abokin sana’arsa Bashir Bala, wanda aka fi sani da Chiroki, ya taimaka wa lokacin da tauraruwarsa ke haskawa a fagen wasan kwaikwayo.

Shi dai mutumin, wanda ke amfani da sunan Doctor Kiyawa, ya nuna rashin jin dadinsa ne kan yadda jaruman Kannywood suka yi watsi da Chiroki duk da bukatar taimakon da yake da ita.

A wata hira da gidan talbijin na Arewa 24 ya yi da shi, Chiroki ya yi ikirarin cewa fardusoshi da jaruman Kannywood sun daina sanya shi a cikin fini-finai lamarin da ya sa a yanzu yake sayar da kunun aya.

Doctor Kiyawa ya yi zargin cewa mata kan shiga harkar fim cikin shekara guda su yi kudi amma mazan da suka kwashe shekara da shekaru suna harkar ba sa samun komai

“A Kannywood ne za ka ga mace ta shigo film wannan shekarar amma ta fi wadda ya yi shekara 10 yana sana’ar film kudi. Ali Nuhu, kai ne wadda yanzu jama’a suke gani da kima a Kannywood, don Allah ku yi wa [Chiroki] wani abu wadda shi ma ba zai manta da kun yi masa halacci ba.”

Sai dai a jerin sakonnin martanin da Ali Nuhu ya mayar wa masu irin wannan korafi ya kalubalance su da su nuna masa irin taimakon da Chiroki ya bai wa Kannywood.

“Zan yi maka tambaya: lokacin da Chiroki yake tashe wa ya yi taimaka wa? Maimakon haka, a kan kudi mene ne ba ya yi wa fardusoshi? Ya kamata mu san abin da muke yi.”

Ya ce bai kamata a rika yi wa ‘yan Kannywood rashin adalci ba wajen dora alhakin gazawar wani daga cikinsu a kansu.

Jarumin ya ce babu wani da ke Kannywood da zai taimaka wa Chiroki, yana mai cewa “ya kamata ya dawo masana’antar ya sasanta da fardusoshi sannan ya ci gaba da aiki kawai.”

More News

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaÆ™i da yiwa tattalin arzikin Æ™asa ne ya hana shi bayyana...

Ƴan sanda sun kama mutane biyu dake samarwa ƴan fashin daji makamai a jihar Kaduna

Rundunar Æ´an sandan jihar Kaduna ta ce tana tsare da wasu mutane biyu da ake zargi da safarar bindiga a jihar. A wata sanarwa ranar...

An kori sojojin Najeriya biyu saboda satar kebul a matatar Dangote

Rundunar sojin Najeriya ta tabbatar da korar wasu sojoji biyu da ake zargi da satar igiyoyin sulke a harabar matatar Dangote da ke jihar...

Magoya bayan APC da dama sun koma NNPP a Kano

Jam'iyar NNPP ta karɓi magoya bayan jam'iyar APC da dama a jihar Kano. Mataimakin gwamnan jihar Kano, Aminu Abdul Salam Gwarzo shi ne ya karɓi...