Chelsea da Tottenham za su buga kwantan wasansu

Chelsea Tottenham

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Hukumar gudanar da gasar Premier ta tsayar da ranar Laraba, domin Chelsea da Tottenham su buga kwantan wasan da suke da shi.

Chelsea za ta karbi bakuncin Brighton & Hove Albion karawar kwantan wasan mako na 27 a gasar ta Premier.

Brighton da Chelsea sun fafata a wasannin bana ranar 16 ga watan Disambar 2018, inda kungiyar Stamford Bridge ta yi nasara da ci 2-1.

Ita kuwa Tottenham za ta karbi bakuncin Crystal Palace a karawar farko da za ta yi a sabon filinta a kwantan wasan mako na 31.

Kungiyoyin biyu sun fafata a Selhurst Park karo biyu a bana, inda aka ci Tottenham 1-0 a Premier ranar 10 ga watan Nuwambar 2018, sannan Palace ta fitar da Tottenham a FA Cup da ci 2-0 ranar 27 ga watan Janairun 2019.

Tottenham tana ta hudu a kan teburin Premier da maki 61, ita kuwa Chelsea tana ta shida da maki 60.

A cikin watan nan na Afirilu ne Tottenham za ta buga wasan daf da na kusa da na karshe da Manchester City a Champions League.

Ita kuwa Chelsea mai buga gasae Europa League za ta fafata ne da SK Slavia Prague a wasan daf da na kusa da na karshe.

More News

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miÆ™ata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaÆ™i da yiwa tattalin arzikin Æ™asa ne ya hana shi bayyana...

Ƴan sanda sun kama mutane biyu dake samarwa ƴan fashin daji makamai a jihar Kaduna

Rundunar Æ´an sandan jihar Kaduna ta ce tana tsare da wasu mutane biyu da ake zargi da safarar bindiga a jihar. A wata sanarwa ranar...