Cece-Kuce Akan Matsayin Nijar a Zaben Najeriya

Mawakan troupe Albishir, na jamhuriyar Nijar sun rera wakar kamfai ga dan takarar jam’iyyar APC a zaben shugaban kasar da za a gudanar a karshen mako a Najeriya, lamarin da tuni ya haifar da mahawara a yanzu haka a bisa yadda mawakan ke kwatanta wakar a matasyin wata gudunmawa daga shugaban kasar Nijar.

Muryar Amurka ta yi kokarin tuntubar jami’an kasar Nijar, domin jin abin da zasu ce kan wannan Magana, amma hakka bata cimma ruwa ba.

Wannan cece-kuce na faruwa ne kwanaki kalilan bayan da aka hango gwamnan jihar Zinder da na Maradi rataye da tutar APC a wuya a ya yin gangamin jam’iyyar na Kano, abin da ya janyo suka daga jam’iyyar adawa ta PDP wacce ke ganin an yi katsalandan.

Tuni dai kungiyoyi masu zaman kansu suka fara jan hankulan ‘yan Nijar a duk inda suke su nisanci kansu daga dukkan wani yunkurin shiga harakokin zabubukan da za a gudanar a ranar Asabar din da ke tafe a Najeriya don kaucewa fadawa tarkon ‘yan siyasa.

Domin cikakken bayani saurari rahotan Sule Muminu Barma.

More News

ÆŠalibai a Jami’ar Jos na zanga-zanga saboda rashin wuta da ruwa

Wasu daliban jami’ar Jos da ke jihar Filato a ranar Alhamis sun gudanar da zanga-zangar nuna rashin amincewarsu da matsalar karancin ruwa da rashin...

MTN yana ƙoƙarin ƙara kuɗin kati da data a Najeriya

Katafaren kamfanin sadarwa na MTN na kokarin kara kudin katin waya da na data a Najeriya. Kamfanin sadarwa mafi girma a nahiyar Afirka ya ba...

Gwamnatin Kano Ta Rage ₦500,000 A Kuɗin Aikin Hajjin Bana

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya sanar da yiwa maniyatan Aikin Hajji da suka fito daga jihar kyautar ₦500,000 domin su cika kuɗin...

Ƴan bindiga sun sace wani limami a jihar Kogi

Ƴan bindiga sun yi garkuwa da Quasim Musa babban limamin garin Iyara dake ƙaramar hukumar Ijumu ta jihar Kogi. Lamarin ya faru ne a ranar...