Buhari ya ji tsoron daga hannun dan takara a Zamfara

Buhari a Zamfara

Image caption

Buhari ya yi kira ga Zamfarawa su zabi wanda suke so

Rikicin ‘yan takarar jam’iyyar APC a Zamfara ya hana shugaba Muhammadu Buhari daga hannun dan takarar gwamna a jihar.

A yayin yakin neman zabensa a Zamfara a ranar Lahadi, Buhari ya ce “duk gardamar da ake idan abu yana wurin shari’a za mu dakata.”

Hakan dai ya kara tabbatar da cewa APC a Zamfara na cike da rudani bayan shugaban ya kasa daga hannun ‘yan takara.

Hukumar zaben kasar INEC ta kara jaddada wa BBC matsayinta cewa APC ba ta da ‘yan takara a zaben 2019 a Zamfara.

Kafin jawabin Buhari, gwamnan jihar mai barin gado Abdulaziz Yari Abubakar ya ce ba za su tilasta wa shugaban daga hannun ‘yan takara ba kamar sauran jihohi.

“Ba za mu tilasta ma sa yin abin da yake da shakku ba.”

“Idan mun tilasta ka cewa sai ka daga hannayen ‘yan takara to muna ganin ba mu yi maka adalci ba saboda kasashen duniya za su kalubalanci matakin domin za a tilasta ka yin wani abin da kotu ba ta bada izinin a yi ba.” In ji shi.

Gwamnan ya ce da yardar Allah da ‘yan takarar APC za a yi zaben 2019.

Tun da farko, a wani gangamin siyasa gwamna Yari ya yi barazanar cewa zabe ba zai yiyu ba idan har babu ‘yan takarar APC.

Ya ce bisa ga hukuncin da kotun Gusau ta zartar, INEC ba ta da hurumin hana wa ‘yan takarar APC shiga zabe, inda ya ce kotun ta yi umurni ga INEC ta karbi ‘yan takarar jam’iyyar.

A cikin jawabinsa a Zamfara, shugaba Buhari ya ce yana fatan kafin ranar Asabar, hukumar zabe za ta fito ta fadi dan takarar da ta yadda da shi.

Sai dai kuma Buhari ya yi kira ga mutane su fito su zabi wanda suke so, a gaban gwamnan Zamfara da ke gawagwarmayar tabbatar da kwamishinansa na kudi a matsayin gwamna.

More News

An kori sojojin Najeriya biyu saboda satar kebul a matatar Dangote

Rundunar sojin Najeriya ta tabbatar da korar wasu sojoji biyu da ake zargi da satar igiyoyin sulke a harabar matatar Dangote da ke jihar...

Magoya bayan APC da dama sun koma NNPP a Kano

Jam'iyar NNPP ta karɓi magoya bayan jam'iyar APC da dama a jihar Kano. Mataimakin gwamnan jihar Kano, Aminu Abdul Salam Gwarzo shi ne ya karɓi...

Sojoji sun gano masana’antar Æ™era bom a jihar Borno

Dakarun rundunar sojan Najeriya sun gano wata masana'anta da mayaƙan kungiyar ISWAP suke ƙera bama-bamai. Masana'antar ƙera bama-bamai an gano ta ne a Abulam-BUK dake...

Atiku ya ziyarci Abdul Ningi

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar ya ziyarci dakataccen ɗan majalisar dattawa sanata, Abdul Ningi dake wakiltar mazaɓar Bauchi ta tsakiya a majalisar dattawa. Atiku...