Shugaban Kungiyar Izala na kasa, Sheikh Abdullahi Bala Lau ya kalubalanci Shugaban Kasa Muhammadu Buhari da gwamnan jihar Kaduna Nasiru El-Rufai da su fito su karyata cewa sun ba wa Malaman Izala motocin alfarma bayan kiran da suka yi wa mabiyansu na cewa su zabi Shugaba Buhari.
A wani sako da kungiyar ta wallafa a shafinta, sun karyata wasu kafar yada labarai na yanar gizo marasa bin gaskiyar labari da suka yada cewa an ba wa Malaman kyautar Motocin alfarma.
Sheikh Bala Lau ya Kara da cewa, kowa ya yi da kyau ya sani.