Kwamitin wanzar da zaman lafiya karkashin jagorancin tsohon shugaban kasar na mulkin soji Abdulsalami Abubakar ne suka shirya taron.
‘Yan takarar biyu sun yi kira ga ‘yan Najeriya da su gudanar da zabe cikin zaman lafiya da lumana da kuma kaucewa duk wani rikici ko hargitsi a lokacin zaben.
Shugaban Najeriyar Muhammadu Buhari, ya bukaci ‘yan Najeriya da su yi wa kasarsu addu’a a daidai lokacin da ake fuskantar zaben da kuma kara tabbatar da hadin kai ga ‘yan kasar baki daya.
Ya kuma bayyana cewa zabe na da matukar amfani domin yana taimakawa wajen samar da zaman lafiya da kuma shirya kasa ta samu ci gaba.
A nasa bangaren, Atiku Abubakar ya yi kalamai irin na tsohon Shugaban Kasar Goodluck Jonathan inda Atikun ya bayyana cewa ba dan Najeriyar da ya kamata ya rasa ransa saboda burinsa na zama shugaban kasa.
Wannan ne karon farko da ‘yan takarar suka zauna wuri daya tun bayan da jam’iyyinsu suka fitar da su a matsayin ‘yan takarar shugabancin kasar.
Buhari dai na neman wa’adi na biyu karkashin jam’iyyar APC yayin da Atiku Abubakar wanda ya taba zama mataimakin shugaban kasa a Najeriyar ke neman shugabancin kasar karkashin jam’iyyar PDP.
Wannan ne karo na biyu da ake sa hannu a irin wannan yarjejeniya duk da cewa Atiku bai halarci yarjejeniyar farko da aka yi ba a shekarar da ta gabata.
Taron sa hannu a yarjejeniyar ya samu halartar tsaffin shuwagabannin kasashen Afirka da jakadun kasashe daban-daban da kuma masu sa ido a harkar zabe.