[ad_1]
Gwamnan jihar Imo Rochas Okorocha, a ranar Laraba da daddare ya ce shugaban kasa,Muhammad Buhari ko kadan baya cikin damuwa kan yadda wasu mutane suke fita daga jam’iyar APC.
Okorocha ya bayyana haka lokacin da yake ganawa da yan jaridun dake fadar shugaban kasa jim kadan bayan da gwamnonin jam’iyar PDP suka yi wata ganawa da Buhari.
Taron ya gudanar a babban dakin taro dake ofishin matar shugaban kasa.
Gwamnoni uku, shugaban majalisar dattawa, Abubakar Bukola Saraki da sanatoci 14 da kuma wasu yan majalisar wakilai 37.
Okorocha ya ce sun gana da shugaban kasar ne domin su tabbatarwa masa da cewa jam’iyar APC har yanzu tana da gwamnoni 22.
[ad_2]