Boko Haram Ta Kai Hari A Kan Sojojin Najeriya A Kusa Da Maiduguri

Wannan harn dai yasa mazauna wannan kauyukan arcewa daga gidajensu zuwa cikin daji dan gudun abin da zai kai ya komo, yayinda aka ce jami’an sojan sun yiwa mahara ba dadi, inda aka ce sun yi shigar burtu irin na sojan suka kuma soma buda wuta kan jami’an sojan, suma jami’an sojan sun maida masu da martani suka kuma ci galaba a kan maharan.

Haka zalika wannan harin ya rutsa da wasu matafiya dake bin wannan hanyar kamar wani da wannan hari ya rutsa da shi a kan hanyarsa na dawowa daga sayan icce a garin na Auno ya yiwa wakilin Muryar Amurka bayani ta wayar tarho. Mutumin yace yanzu haka kowa na ta kansa ne ya tsira da rayuwarsa.

Wakilin Sashen Hausa Haruna Dauda ya ci gaba da tattaunawa da wasu da suka arce suka buya a ciki daji bayan wasu sun fada masa bindiga ta kama wani kuma tuni an kai shi asibiti. Wani da ya gudu da ransa ya shaida mana cewa maharan da sojojin sun yi bata kashi kuma haka ne ya yi sanadiyar mazauna kauyen suka shiga daji.

Wannan lamari yana aukuwa ne a daidai lokacin da wani kwamiti mai karfin gaske karkshin jagorancin gwamnan jihar Borno Ukasha Shattima uka aikawa shugaba Muhammadu Buhari rahoto a kan halin da ake ciki game da tsaron jihar Borno.

Ga rahoton da Haruna Dauda ya aiko mana daga Maiduguri:

More News

MTN yana ƙoƙarin ƙara kuɗin kati da data a Najeriya

Katafaren kamfanin sadarwa na MTN na kokarin kara kudin katin waya da na data a Najeriya. Kamfanin sadarwa mafi girma a nahiyar Afirka ya ba...

Gwamnatin Kano Ta Rage ₦500,000 A Kuɗin Aikin Hajjin Bana

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya sanar da yiwa maniyatan Aikin Hajji da suka fito daga jihar kyautar ₦500,000 domin su cika kuɗin...

Ƴan bindiga sun sace wani limami a jihar Kogi

Ƴan bindiga sun yi garkuwa da Quasim Musa babban limamin garin Iyara dake ƙaramar hukumar Ijumu ta jihar Kogi. Lamarin ya faru ne a ranar...

Delta: An dawo da gawarwakin sojojin da aka kashe Abuja don yi musu jana’iza

Gawarwakin sojojin da aka kashe a jihar Delta kwanan nan sun isa maƙabartar sojoji ta kasa da ke Abuja. Gawarwakin sun iso ne da misalin...