‘Yan sanda a birnin Maiduguri a jihar Borno a Najeriya sun tabbatar da cewa kungiyar Boko Haram ta hallaka mutane 11 da kuma raunata wasu 15.
Wani shugaban kungiyar mayakan sa-kai ya bayyana cewa an kai harin ne da nufin dakatar da mutane zuwa rumfunan zabe.
Harin ya faru ne da safiyar Asabar a kudancin birnin, inda mayakan suka bude wuta, wasu ‘yan kunar bakin-wake kuma suka tarwatsa kansu da bama-bamai.
A yau ne aka shirya gudanar da zaben shugaban kasa da na ‘yan majalisar dokokin kasar, sai dai an dage zaben zuwa mako mai zuwa sa’o’i kadan kafin a fara kada kuri’a.
Aikace-aikacen ‘yan ta’adda ya tilasta wa mutane da dama barin muhallansu a Borno, al’amarin da ya jawo hukumar zabe ta kirkiri rumfunan zabe a sansanonin ‘yan gudn hijira.
Ko a ranar Laraba da ta gabata ‘yan Boko Haram sun far wa ayarin motocin gwamnan Borno, inda suka kashe mutum uku.