Boko Haram ta hallaka mutum 11 a Maiduguri

'Yan sanadan kwantar da tarzoma a Najeriya

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Image caption

‘Yan sanda a birnin Maiduguri a jihar Borno a Najeriya sun tabbatar da cewa kungiyar Boko Haram ta hallaka mutane 11 da kuma raunata wasu 15.

Wani shugaban kungiyar mayakan sa-kai ya bayyana cewa an kai harin ne da nufin dakatar da mutane zuwa rumfunan zabe.

Harin ya faru ne da safiyar Asabar a kudancin birnin, inda mayakan suka bude wuta, wasu ‘yan kunar bakin-wake kuma suka tarwatsa kansu da bama-bamai.

A yau ne aka shirya gudanar da zaben shugaban kasa da na ‘yan majalisar dokokin kasar, sai dai an dage zaben zuwa mako mai zuwa sa’o’i kadan kafin a fara kada kuri’a.

Aikace-aikacen ‘yan ta’adda ya tilasta wa mutane da dama barin muhallansu a Borno, al’amarin da ya jawo hukumar zabe ta kirkiri rumfunan zabe a sansanonin ‘yan gudn hijira.

Ko a ranar Laraba da ta gabata ‘yan Boko Haram sun far wa ayarin motocin gwamnan Borno, inda suka kashe mutum uku.

More News

EFCC na neman Yahaya Bello ruwa a jallo

Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (Economic and Financial Crimes Commission) ta bayyana tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello a matsayin...

Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a...

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon ĆŠaya Daga Cikin Ćłan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon É—aya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...