Boko Haram ta hallaka mutum 11 a Maiduguri

'Yan sanadan kwantar da tarzoma a Najeriya

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Image caption

‘Yan sanda a birnin Maiduguri a jihar Borno a Najeriya sun tabbatar da cewa kungiyar Boko Haram ta hallaka mutane 11 da kuma raunata wasu 15.

Wani shugaban kungiyar mayakan sa-kai ya bayyana cewa an kai harin ne da nufin dakatar da mutane zuwa rumfunan zabe.

Harin ya faru ne da safiyar Asabar a kudancin birnin, inda mayakan suka bude wuta, wasu ‘yan kunar bakin-wake kuma suka tarwatsa kansu da bama-bamai.

A yau ne aka shirya gudanar da zaben shugaban kasa da na ‘yan majalisar dokokin kasar, sai dai an dage zaben zuwa mako mai zuwa sa’o’i kadan kafin a fara kada kuri’a.

Aikace-aikacen ‘yan ta’adda ya tilasta wa mutane da dama barin muhallansu a Borno, al’amarin da ya jawo hukumar zabe ta kirkiri rumfunan zabe a sansanonin ‘yan gudn hijira.

Ko a ranar Laraba da ta gabata ‘yan Boko Haram sun far wa ayarin motocin gwamnan Borno, inda suka kashe mutum uku.

More News

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miÆ™ata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaÆ™i da yiwa tattalin arzikin Æ™asa ne ya hana shi bayyana...

Ƴan sanda sun kama mutane biyu dake samarwa ƴan fashin daji makamai a jihar Kaduna

Rundunar Æ´an sandan jihar Kaduna ta ce tana tsare da wasu mutane biyu da ake zargi da safarar bindiga a jihar. A wata sanarwa ranar...