Jami’an kula da gidan namun daji na zoo da ke Kano sun ce suna bincike kan wani goggon biri da ya cinye naira miliyan bakwai.
Shugaban gidan zoo din Umar Kashekobo ya ce: “‘Yan sanda na bincike kan ainihin abin da ya fau – abin da zan iya cewa kawai shi ne kudi sun bata.”
Mai magana da yawun ‘yan sandar jihar Abdullahi Kiyawa ya ce kudaden shiga gidan zoo din na kwana biyar ne suka yi batan dabo.
Ya shaida wa BBC cewa zuwa yanzu an kama mutum 10 kuma jami’ai na binciken abin da ya sa ake ajiye kudi mai yawa haka ba tare da kai su banki ba.
A farkon makon nan gidan rediyon Freedom a Kanon ya sanar da bacewar kudin.
Gidan rediyon ya yi hira da wani ma’aikacin bangaren kudi na gidan wanda ya ce goggon birin ya sulale ya shiga cikin ofishin ne ya sace kudaden tare da cinye su.
A shekarar da ta gabata ma wata ma’aikaciya a hukumar shirya jarabawar shiga jami’a ta Jamb reshen jihar Benue, ta ce wani maciji ya shiga ofishin ya hadiye naira miliyan 36 kudin jarabawar da aka tara.
Makonni kadan da suka gabata ita da wasu jami’an suka musanta hannu a batan kudin.