Sashen Turancin broka wato BBC Pidgin ya kaddamar da gasar rubutun zube da harshen Pidgin a ranar Alhamis 1 ga watan Agustan 2019.
Gasar a bude take ga dukkanin daliban manyan makarantun gaba da sakandare a nahiyar Afirka.
Masu sha’awar shiga gasar za su rubuta makala ne mai kalmomin da ba su wuce 800 ba kan maudu’in “ko mace za ta iya jagorancin siyasa a nahiyar Afirka?” (“Is Africa ready for female political leadership?”).
Wani rukunin alkalai da suka hada da malamai da ‘yan jarida da marubuta na harshen Pidgin wadanda suka fito daga Afirka ta Yamma ne za su zabi mutum daya wanda ya yi nasara.
Wajibi ne kowacce makala ta dace da tsarin harshen Pidgin tare da bin ka’idojin rubutu.
Za a sanar da wanda ya yi nasarar ne a Legas ranar 20 ga watan Satumban 2019. Sannan za a ba shi kyautar dala $500 (kusan naira 180,000)
Za a rufe shiga gasar ne a ranar Juma’a 30 ga watan Agustan 2019.
A aiko da makala zuwa adireshin imel na bbcpidgin.essay@bbc.co.uk