BBC ta bude gasar rubutu a harshen Pidgin | BBC Hausa

Wani likita yana rubutu da biro kan takarda

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Image caption

Za a lashe kyautar sama da naira 180,000

Sashen Turancin broka wato BBC Pidgin ya kaddamar da gasar rubutun zube da harshen Pidgin a ranar Alhamis 1 ga watan Agustan 2019.

Gasar a bude take ga dukkanin daliban manyan makarantun gaba da sakandare a nahiyar Afirka.

Masu sha’awar shiga gasar za su rubuta makala ne mai kalmomin da ba su wuce 800 ba kan maudu’in “ko mace za ta iya jagorancin siyasa a nahiyar Afirka?” (“Is Africa ready for female political leadership?”).

Wani rukunin alkalai da suka hada da malamai da ‘yan jarida da marubuta na harshen Pidgin wadanda suka fito daga Afirka ta Yamma ne za su zabi mutum daya wanda ya yi nasara.

Wajibi ne kowacce makala ta dace da tsarin harshen Pidgin tare da bin ka’idojin rubutu.

Za a sanar da wanda ya yi nasarar ne a Legas ranar 20 ga watan Satumban 2019. Sannan za a ba shi kyautar dala $500 (kusan naira 180,000)

Za a rufe shiga gasar ne a ranar Juma’a 30 ga watan Agustan 2019.

A aiko da makala zuwa adireshin imel na bbcpidgin.essay@bbc.co.uk

More News

EFCC na neman Yahaya Bello ruwa a jallo

Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (Economic and Financial Crimes Commission) ta bayyana tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello a matsayin...

Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a...

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon ĆŠaya Daga Cikin Ćłan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon É—aya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...