Ban ce Buhari ya sauka daga kujerar mulkinsa ba – IBB

Janar Ibrahim Badamasi Babangida, tsohon shugaban mulkin soja, ya yi watsi da labaran da ake yadawa ta kafar Intanet dake cewa ya shawarci shugaban kasa Muhammad Buhari ya sauka daga kan mulki.

Babangida a wata sanarwa da ofishinsa na yada labarai ya fitar ta bayyana cewa tsohon shugaban kasar bai mallaki wani shafi ba na kafafen sadarwar zamani ballantana ya yi amfani da kafar wajen bayyana ra’ayinsa kan abinda ke faruwa a ƙasarnan.

Sanarwar ta ce an jawo hankalin tsohon shugaban kasar kan wani shafi na kafar sadarwar Twitter da kuma sauran kafafen sadarwar zamani mai dauke da suna tsohon shugaban kasar.

Ta kuma shawarci jama’a musamman masu amfani da kafar sadarwar zamani ta Twitter cewa tsohon shugaban bashi da shafi a kafar ko kuma kowace kafar sadarwar zamani.

More News

EFCC na neman Yahaya Bello ruwa a jallo

Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (Economic and Financial Crimes Commission) ta bayyana tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello a matsayin...

Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a...

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon ĆŠaya Daga Cikin Ćłan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon É—aya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...