Ban ce Buhari ya sauka daga kujerar mulkinsa ba – IBB

Janar Ibrahim Badamasi Babangida, tsohon shugaban mulkin soja, ya yi watsi da labaran da ake yadawa ta kafar Intanet dake cewa ya shawarci shugaban kasa Muhammad Buhari ya sauka daga kan mulki.

Babangida a wata sanarwa da ofishinsa na yada labarai ya fitar ta bayyana cewa tsohon shugaban kasar bai mallaki wani shafi ba na kafafen sadarwar zamani ballantana ya yi amfani da kafar wajen bayyana ra’ayinsa kan abinda ke faruwa a ƙasarnan.

Sanarwar ta ce an jawo hankalin tsohon shugaban kasar kan wani shafi na kafar sadarwar Twitter da kuma sauran kafafen sadarwar zamani mai dauke da suna tsohon shugaban kasar.

Ta kuma shawarci jama’a musamman masu amfani da kafar sadarwar zamani ta Twitter cewa tsohon shugaban bashi da shafi a kafar ko kuma kowace kafar sadarwar zamani.

More News

ÆŠalibai a Jami’ar Jos na zanga-zanga saboda rashin wuta da ruwa

Wasu daliban jami’ar Jos da ke jihar Filato a ranar Alhamis sun gudanar da zanga-zangar nuna rashin amincewarsu da matsalar karancin ruwa da rashin...

MTN yana ƙoƙarin ƙara kuɗin kati da data a Najeriya

Katafaren kamfanin sadarwa na MTN na kokarin kara kudin katin waya da na data a Najeriya. Kamfanin sadarwa mafi girma a nahiyar Afirka ya ba...

Gwamnatin Kano Ta Rage ₦500,000 A Kuɗin Aikin Hajjin Bana

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya sanar da yiwa maniyatan Aikin Hajji da suka fito daga jihar kyautar ₦500,000 domin su cika kuɗin...

Ƴan bindiga sun sace wani limami a jihar Kogi

Ƴan bindiga sun yi garkuwa da Quasim Musa babban limamin garin Iyara dake ƙaramar hukumar Ijumu ta jihar Kogi. Lamarin ya faru ne a ranar...