APC ta dakatar da Amosun da Okorocha

Hukumar jam’iyyar APC ta kasa ta dakatar da gwamnan jihar Ogun, Ibikunle Amosu da kuma Rochas Okorocha na jihar Imo.

Har ila yau shugabancin jam’iyar ya bawa kwamitin zartarwar ta shawarar korar su daga jam’iyar baki daya.

Shugabancin jam’iyyar ya cimma wannan matsaya ne a wani taro da ya gudanar ranar juma’a a Abuja inda aka zargi mutanen biyu da laifin yin zagon kasa ga jam’iyar.

Dukkanin mutanen biyu sun lashe zaben kujerar sanata karkashin jam’iyar a zaben da ya gabata na ranar Asabar.

Sun raba gari ne da shugabancin jam’iyyar APC na kasa bayan da yan takarar da su ke goyon baya su gaje su suka gaza samun tikitin takara a jam’iyarts ta APC.

Yayin da Okorocha ke goyon bayan surukinsa, Uche Nwosu a matsayin mutumin da zai gaje shi a daya bangaren Amosu na goyon bayan Adekunle Akinlade wanda wakili ne a majalisar wakilai ta tarayya.

Akinlade na takara a jam’iyar APM ya yin da Nwosu ke takara a jam’iyar AA.

More News

APC ta dakatar da Ganduje a matakin gunduma

Mambobin jam'iyyar APC a mazabar da ke Karamar Hukumar Dawakin Tofa a Jihar Kano sun dakatar da Shugaban Jam’iyyar APC na kasa Abdullahi Ganduje. ...

Wani mutumi ya kashe mahaifiyarsa a kan kudi

Jami’an rundunar ‘yan sandan jihar Osun sun kama wani mazaunin kauyen Kajola da ke kusa da Apomu a jihar mai suna Lukman Adejoju bisa...

Mayaƙan Boko Haram Biyu Sun Miƙa Kansu Ga Sojoji

Rundunar dakarun soja ta ƙasa da ƙasa wato Multi National Task Force(MNJTF) a turance shiya ta 3 dake Monguno a Najeriya ta bayar da...

Sojoji a birnin Ibadan  sun kama Æ´an fafutukar kafa Æ™asar Oduduwa

Dakarun rundunar sojan Najeriya  sun samu nasarar kama wasu mutane masu fafutukar kafa ƙasar Oduduwa a birnin Ibadan na jihar Oyo. Masu fafutukar sanye da...