Farfesa Mahmoud Yakubu, Shugaban hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa, INEC, ya ce an yi yunkurin kawowa hukumar zagon kasa a shirye shiryen da take na zaben 2019.
Ya fadi haka ne a Abuja lokacin da yake karin haske kan dalilin da yasa hukumar ta dage zaben shugaban kasa da aka shirya gudanarwa yau Asabar.
A yanzu dai an kara mako guda kan zaben shugaban kasar haka ma abin yake ga zaben gwamnoni da kuma yan majalisun dokokin jihohi.
Yakubu ya ce dage zaben bashi da alaka da rashin kwarewa,matsalar tsaro ko kuma tsoma baki daga wani bangare na siyasa.
Ya lissafo gobarar da ta tashi a ofisoshin hukumar dake wasu kananan hukumomi a jihohin, Plataeu, Abia da Anambra inda ya ce hukumar ta yi iya bakin kokarinta wajen shawo kan waÉ—annan matsaloli.