An yi jana’izar mutum 19 a Jigawa

FRSC

An yi jana’izar mutum 19 da suka mutu sanadiyyar wani hadarin mota a karamar hukumar Gwaram da ke jihar Jigawa ranar Laraba.

Hadarin ya faru ne a garin Gwaram Sabuwa da misalin karfe 11:30 na dare, bayan da tayar gaban motar da ke dauke da fasinjoji 40 ta fashe.

Rahotanni sun ce daga nan ne sai motar ta wuntsula kafin ta kama da wuta. Mutum 21 daga cikin fasinjojin ne dai suka ji rauni.

Wani da abin ya faru a kan idonsa ya ce gawarwakin fasinjojin sun kone “kurumus ta yadda ba za a iya gane su ba.”

“Na ga gawarwakin jarirai shida tare da gawarwakin iyayensu,” in ji shi.

Mutanen da hadarin ya rutsa da su wadanda galibinsu mata ne da kananan yara suna kan hanyarsu ta dawowa daga daurin aure ne.

More News

ÆŠalibai a Jami’ar Jos na zanga-zanga saboda rashin wuta da ruwa

Wasu daliban jami’ar Jos da ke jihar Filato a ranar Alhamis sun gudanar da zanga-zangar nuna rashin amincewarsu da matsalar karancin ruwa da rashin...

MTN yana ƙoƙarin ƙara kuɗin kati da data a Najeriya

Katafaren kamfanin sadarwa na MTN na kokarin kara kudin katin waya da na data a Najeriya. Kamfanin sadarwa mafi girma a nahiyar Afirka ya ba...

Gwamnatin Kano Ta Rage ₦500,000 A Kuɗin Aikin Hajjin Bana

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya sanar da yiwa maniyatan Aikin Hajji da suka fito daga jihar kyautar ₦500,000 domin su cika kuɗin...

Ƴan bindiga sun sace wani limami a jihar Kogi

Ƴan bindiga sun yi garkuwa da Quasim Musa babban limamin garin Iyara dake ƙaramar hukumar Ijumu ta jihar Kogi. Lamarin ya faru ne a ranar...