An yi jana’izar mutum 19 a Jigawa

FRSC

An yi jana’izar mutum 19 da suka mutu sanadiyyar wani hadarin mota a karamar hukumar Gwaram da ke jihar Jigawa ranar Laraba.

Hadarin ya faru ne a garin Gwaram Sabuwa da misalin karfe 11:30 na dare, bayan da tayar gaban motar da ke dauke da fasinjoji 40 ta fashe.

Rahotanni sun ce daga nan ne sai motar ta wuntsula kafin ta kama da wuta. Mutum 21 daga cikin fasinjojin ne dai suka ji rauni.

Wani da abin ya faru a kan idonsa ya ce gawarwakin fasinjojin sun kone “kurumus ta yadda ba za a iya gane su ba.”

“Na ga gawarwakin jarirai shida tare da gawarwakin iyayensu,” in ji shi.

Mutanen da hadarin ya rutsa da su wadanda galibinsu mata ne da kananan yara suna kan hanyarsu ta dawowa daga daurin aure ne.

More News

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miÆ™ata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaÆ™i da yiwa tattalin arzikin Æ™asa ne ya hana shi bayyana...

Ƴan sanda sun kama mutane biyu dake samarwa ƴan fashin daji makamai a jihar Kaduna

Rundunar Æ´an sandan jihar Kaduna ta ce tana tsare da wasu mutane biyu da ake zargi da safarar bindiga a jihar. A wata sanarwa ranar...