An samu biliyoyin kudade, manyan bindigu da dubban katinan zabe a gidan Lawal Daura

[ad_1]








A wani rahoton da jaridar Newsbreakng ta wallafa a jiya asabar yace, an gano makudan kudade har Naira biliyan 21 a gidan tsohon shugaban hukumar jami’an tsaro na farin kaya (DSS), Mallam Lawal Musa Daura dake babban birnin tarayya, Abuja.

Wata majiya dake da masaniya kan lamarin tayi ikirarin cewa an gano bindigogi sama da 4000 tare da wasu kananan makamai da kuma katin zabe mallakar wasu bakin haure daga jamhuriyar Nijar duk a gidan nasa.

Ana tuhumar tsohon shugaban DSS din da karkatar da wasu makuden kudade har dala milyan 21 da ya gada daga tsohon shugaban hukumar DSS, Mr Ita Ekpenyong.

A halin yanzu Daura na amsa tambayoyi game da kudin pansho N12.9 biliyan da aka fitar daga asusun ajiya ta hukumar na DSS.

Ana kuma tuhumarsa da hannu cikin cire N1.6 biliyan daga asusun ajiyar inshora na ma’aikatan hukumar, inji majiyar.

Sai dai babu wata kwakkwarar majiya daga hukumar data tabbatar da afkuwar wannan lamarin saboda babu wanda yake son yin tsokaci akan wannan babban batu irin wanda daya shafi tsohon shugaban hukumar ta DSS.

A ranar Alhamis data gabata, tsohon shugaban hukumar DSS, Ekpenyong ya bayyana a hedkwatar hukumar EFCC inda ya amsa tambayoyi kan yadda ya sarrafa kudaden da tsohon mai bawa shugaban kasa shawara kan tsaro, Kanal Sambo Dasuki, ya bashi gabanin zaben shekarar 2015.




[ad_2]

More News

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon Ɗaya Daga Cikin Ƴan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon É—aya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...

Gwamnatin Tarayya Za Ta Fara Rabon Gidaje 8925

Gwamnatin tarayya ta ce ta fara raba gidaje 8925  ga mutanen da suka nema kuma suka cancanci a basu a faɗin ƙasa baki ɗaya...

Ƴan Bindiga A Zamfara Sun Kashe Sakataren Jam’iyar PDP

Wasu ƴan bindiga da ba a san ko suwaye ba sun kashe, Musa Ille  sakataren jam'iyar PDP na ƙaramar hukumar Tsafe a jihar Zamfara. Zagazola...