An sami gawar dan kasar Lebanon da aka yi garkuwa da shi a Kano

‘Yan sanda a Jihar Kano sun samu samo gawar wani Injiniyan gine-gine dan kasar Lebanon wanda aka yi garkuwa da shi ranar Talata.

Wasu yan bindiga da ba’asan ko suwaye ba sune suka yi garkuwa da marigayin da safiyar ranar Talata lokacin da yake duba aikin titin kasa da ake yi a shatale-talen Dangi a cikin birnin Kano.

Ya yin da aka kashe direbansa nan take a wurin shi kuwa anyi awon gaba da shi ya zuwa wani da ba a sani ba.

Marigayin na aiki ne da kamfanin gine-gine na Triacta.

Da yake tabbatar da mutuwarsa mai magana da yawun rundunar yansandan jihar, Abdullahi Haruna ya ce an gano gawar Injiniyan ne akan hanyar Kano zuwa Maiduguri da yammacin ranar Alhamis.

Abdullahi ya kara da cewa ba a kama kowa ba game da lamarin amma rundunar na cigaba da gudanar da bincike.

More News

APC ta dakatar da Ganduje a matakin gunduma

Mambobin jam'iyyar APC a mazabar da ke Karamar Hukumar Dawakin Tofa a Jihar Kano sun dakatar da Shugaban Jam’iyyar APC na kasa Abdullahi Ganduje. ...

Wani mutumi ya kashe mahaifiyarsa a kan kudi

Jami’an rundunar ‘yan sandan jihar Osun sun kama wani mazaunin kauyen Kajola da ke kusa da Apomu a jihar mai suna Lukman Adejoju bisa...

Mayaƙan Boko Haram Biyu Sun Miƙa Kansu Ga Sojoji

Rundunar dakarun soja ta ƙasa da ƙasa wato Multi National Task Force(MNJTF) a turance shiya ta 3 dake Monguno a Najeriya ta bayar da...

Sojoji a birnin Ibadan  sun kama Æ´an fafutukar kafa Æ™asar Oduduwa

Dakarun rundunar sojan Najeriya  sun samu nasarar kama wasu mutane masu fafutukar kafa ƙasar Oduduwa a birnin Ibadan na jihar Oyo. Masu fafutukar sanye da...