An sake samun ƴan daba da suka tuba a Kano

Wasu sabbin ’yan daba 43 (Yan Daba) daga daga yankin Goburawa-Gangare da Tudun Fulani Quarters na karamar hukumar Ungogo ta Jihar Kano sun rungumi zaman lafiya tare da mika kansu ga rundunar ‘yan sandan jihar.

‘Yan barandan 43 sun sa adadin tubabbun ‘yan baranda a Jihar zuwa 143. ‘Yan barandan sun kasance tare da wasu dattijai, masu ruwa da tsaki a cikin al’umma.

Kakakin rundunar ‘yan sandan, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, a wata sanarwa da ya raba wa manema labarai, ya bayyana cewa wadannan ‘yan daba 43 na kungiyoyin biyu a baya sun yi artabu da juna (Fadan Yan Daba) sama da shekaru biyar.

Sanarwar ta ce, fadan ya kan kai ga kai hare-hare kan mutanen da ba su ji ba ba su gani ba, wanda ke haddasa asarar rayuka, da jikkatar mutane, da kuma asarar dukiyoyi.

More News

An samu ambaliyar ruwa a Adamawa

Anguwan Tana, al’ummar karamar hukumar Yola ta Arewa, sun shiga tasgaro a ranar Alhamis sakamakon ambaliya daga kogin Kilange da kogin Faro. Mazaunan garin...

Sojoji sun ceto mutane 6 daga cikin ɗaliban jami’ar Gusau da aka sace

Sojoji sun ceto dalibai mata shida daga cikin daliban Jami'ar Gwamnatin Tarayya dake Gusau da aka bada rahoton yan bindiga sun yi garkuwa da...

Ƴan bindiga sun yi garkuwa da ɗaliban Jami’ar Tarayya da ke Gusau

An sace wasu daliban jami’ar tarayya ta Gusau da ba a tantance adadinsu ba da sanyin safiyar Juma’a. ‘Yan ta’addan masu yawan gaske sun...

Ƴan sanda sun kama masu safarar makamai wa ƴan bindiga

Jami’an hukumar ‘yan sanda reshen Karasuwa a jihar Yobe sun cafke wasu mutane biyu da ake zargi da kai wa ‘yan bindiga makamai da...