An rufe filin jirgin saman Seattle bayan da wani ya sace jirgin sama

[ad_1]

Na’urarku na da matsalar sauraren sauti

Ana iya ganin jiragen yaki na bin jirgin

Wani ma’aikacin kamfanin jirgin sama ya sace wani jirgin fasinja daga filin jirgin sama na birnin Seattle a Amurka, kuma jirgin ya fadi a wani tsibiri dake kusa.

Jami’ai a filin jirgin saman sun ce mutumin da ya sace jirgin a jiya Jumma’a, ya tashi da shi ne ba tare da izini ba.

A sanadiyyar aukuwar wannan lamarin an rufe filin jirgin sama na Seattle-Tacoma International.

Wasu jiragen yaki biyu samfurin F-15 sun bi jirgin wanda daga baya ya fado a Puget Sound. Jami’ai sun ce da alama matukin jirgin ya mutu nan take.

Ofishin ‘yan sandan garin ya ce lamarin “ba aikin ta’addanci ba ne”, kuma sun ce mutumin mai shekara 29 da haihuwa sananne ne a garesu.

Jirgin samfurin Bombardier Q400 mai injuna biyu mallakin kamfanin Horizon Air ne.

An tura wasu jiragen yaki biyu nan take, kuma bidiyon da wasu ‘yan kallo suka nada na nuna jiragen yakin na bin jirgin da aka sace.

Shin me yasa ya saci jirgin?

Ana ganin mutumin da ya saci jirgin yayi haka ne saboda ya burge kawai.

Sautin da jami’ai suka nada a lokacin da suke magana da mutumin ya tabbatar da haka.

An kuma ji mutumin na nuna damuwarsa saboda rashin isasshen mai a cikin jirgin.

Hakkin mallakar hoto
AFP

Image caption

Wannan hoton jirgin ne yana tafiya kasa-kasa kusa da ruwa

Ya kuma ce zai iya sauka da jirgin da kansa saboda ya iya “tuka jiragen sama na cikin wasannin komfuta”.

A cikin sautin an kuma ji mutumin na cewa:

  • Ya na sha’awar zuwa dutsen Olympic Mountain da ke jihar Washington domin ya sha kallo
  • Ko zai iya yin wasa da jujjuya jigin kamar mazari kafin ya sauka
  • Yana fatan kamfanin da suka mallaki jirgin za su dauke shi aiki a matsayin direban jirgi idan har ya koma da jirgin ba tare da wata matsala ba

Hakkin mallakar hoto
CBS

Image caption

Hoton inda jirgin ya fadi kuma ya kama da wuta

[ad_2]

More News

EFCC na neman Yahaya Bello ruwa a jallo

Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (Economic and Financial Crimes Commission) ta bayyana tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello a matsayin...

Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a...

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon ĆŠaya Daga Cikin Ćłan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon É—aya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...