An Harbe Dan Takarar Sanata A Jihar Oyo

A jiya Asabar ne wasu mutane da kawo iyanzu ba’a san ko su wanene ba suka harbe dan takarar sanata a tutar jam’iyyar African development party, wato ADP, Hon. Temitope Olatoye, da aka fi sani da suna “Sugar”, a kauyen Elesu Lalupon, a cikin karamar hukumar Lagelu.

Temitope Olatoye Sugar shine mai wakiltar mazabar Lagelu da Akinyele daga jihar Oyo, a majalisar wakilan tarayyar Najeriya.

Kwamishinan ‘yan sandan jihar Oyo Mr. Shina Olukolu, ya tabbatar da kisan, yace kawo yanzu basu kama kowa ba, amma suna aiki tukuru don gano wadanda suka aikata wannan aiki.

Kwamishinan ‘yan sandan na jihar Oyo ya cewa basason suyi shaci fadi a halin yanzu, kuma ko akwai wadanda suke zargi ba zasu fadi ba, saboda kada su ranta a na kare, Mr. Shina Olukolu ya kara da cewa jama’a su sani cewa komai dadewa zasu kama wadanda sukayi kisan, kuma yace jama’a suyi hakuri kada suyi wani abu da zai tada zauna tsaye.

Jama’ar garin sun nuna rashin jin dadin su, akan kisan da akayi wa “Sugar”.

More News

EFCC na neman Yahaya Bello ruwa a jallo

Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (Economic and Financial Crimes Commission) ta bayyana tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello a matsayin...

Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a...

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon Ɗaya Daga Cikin Ƴan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon ɗaya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...