An gama aikin ceto mutanen da ke ƙarƙashin ginin benen da ya rufta a Lagos

Shugaban hukumar bada agajin gaggawa ta jihar Lagos, LASEMA, Adesina Tiamiyu, ya ce ya zuwa yanzu babu wani mutum da ya rage cikin baraguzan ginin bene mai hawa uku da ya ruguzo a yankin Ita Faji dake jihar.

Tiamiyu ya bayyana haka lokacin da yake magana da yan jaridu a wurin da lamarin yafaru.

“Mun dakatar da aiki da misalin karfe uku na dare bayan da muka zakulo gawar wani mutum, mun tabbata cewa babu wanda yayi saura karkarshin baraguzan ginin,” ya ce.

Amma wasu mazauna yankin sun musalta ikirarin na shugaban hukumar ta LASEMA inda suka dage kan cewa har yanzu akwai sauran mutane da suka rage a karkashin baraguzan ginin.

Ginin benen mai hawa uku dake ɗauke da makarantar firamare a hawa na biyu ya rufta ranar Laraba da safe lokacin da dalibai suke tsaka da karatu cikin ajinsu.

Akalla mutane 12 ciki har da yara tara aka tabbatar da mutuwarsu.

More News

An kori sojojin Najeriya biyu saboda satar kebul a matatar Dangote

Rundunar sojin Najeriya ta tabbatar da korar wasu sojoji biyu da ake zargi da satar igiyoyin sulke a harabar matatar Dangote da ke jihar...

Magoya bayan APC da dama sun koma NNPP a Kano

Jam'iyar NNPP ta karɓi magoya bayan jam'iyar APC da dama a jihar Kano. Mataimakin gwamnan jihar Kano, Aminu Abdul Salam Gwarzo shi ne ya karɓi...

Sojoji sun gano masana’antar ƙera bom a jihar Borno

Dakarun rundunar sojan Najeriya sun gano wata masana'anta da mayaƙan kungiyar ISWAP suke ƙera bama-bamai. Masana'antar ƙera bama-bamai an gano ta ne a Abulam-BUK dake...

Atiku ya ziyarci Abdul Ningi

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar ya ziyarci dakataccen ɗan majalisar dattawa sanata, Abdul Ningi dake wakiltar mazaɓar Bauchi ta tsakiya a majalisar dattawa. Atiku...