An gama aikin ceto mutanen da ke ƙarƙashin ginin benen da ya rufta a Lagos

Shugaban hukumar bada agajin gaggawa ta jihar Lagos, LASEMA, Adesina Tiamiyu, ya ce ya zuwa yanzu babu wani mutum da ya rage cikin baraguzan ginin bene mai hawa uku da ya ruguzo a yankin Ita Faji dake jihar.

Tiamiyu ya bayyana haka lokacin da yake magana da yan jaridu a wurin da lamarin yafaru.

“Mun dakatar da aiki da misalin karfe uku na dare bayan da muka zakulo gawar wani mutum, mun tabbata cewa babu wanda yayi saura karkarshin baraguzan ginin,” ya ce.

Amma wasu mazauna yankin sun musalta ikirarin na shugaban hukumar ta LASEMA inda suka dage kan cewa har yanzu akwai sauran mutane da suka rage a karkashin baraguzan ginin.

Ginin benen mai hawa uku dake ɗauke da makarantar firamare a hawa na biyu ya rufta ranar Laraba da safe lokacin da dalibai suke tsaka da karatu cikin ajinsu.

Akalla mutane 12 ciki har da yara tara aka tabbatar da mutuwarsu.

More News

EFCC na neman Yahaya Bello ruwa a jallo

Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (Economic and Financial Crimes Commission) ta bayyana tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello a matsayin...

Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a...

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon Ɗaya Daga Cikin Ƴan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon ɗaya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...