An É—age sauraron shari’ar Hadizan Gabon

Khadi Rilawanu Kyaudai na kotun shari’ar musulunci dake zamanta a Magajin Gari Zariya,ya dage shari’ar da yake sauraro tsakanin yar wasan Kannywood, Hadiza Gabon da Kuma Wani ma’aikacin gwamnati mai suna Bala Musa.

Ana tuhumar Gabon da laifin zanbatar Bala bayan da ta karɓe masa yan kudade da sunan zata aure shi.

An dage zaman shari’ar zuwa ranar, 1 ga watan Agusta biyo bayan yanayin rashin lafiya da matar alkalin take ciki.

Musa ya kai karar ne inda yake bukatar jaruma Gabon ta dawo masa da kudinsa,396,000 bayan da taki amincewa ta aure shi.

Tuni dai jarumar ta musalta cewa akwai wannan alƙawari a yayin zaman kotun da aka yi na farko a ranar 14 ga watan Yuni.

Jaridar Daily Trust ta rawaito cewa bayan da kowa ya gama hallara domin fara sauraren shari’ar na ranar Talata sai alkalin ya sanar cewa ya samun labarin an kai É—aya daga cikin matansa a asibiti.

More News

EFCC na neman Yahaya Bello ruwa a jallo

Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (Economic and Financial Crimes Commission) ta bayyana tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello a matsayin...

Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a...

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon ĆŠaya Daga Cikin Ćłan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon É—aya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...