An ɗage sauraron shari’ar Hadizan Gabon

Khadi Rilawanu Kyaudai na kotun shari’ar musulunci dake zamanta a Magajin Gari Zariya,ya dage shari’ar da yake sauraro tsakanin yar wasan Kannywood, Hadiza Gabon da Kuma Wani ma’aikacin gwamnati mai suna Bala Musa.

Ana tuhumar Gabon da laifin zanbatar Bala bayan da ta karɓe masa yan kudade da sunan zata aure shi.

An dage zaman shari’ar zuwa ranar, 1 ga watan Agusta biyo bayan yanayin rashin lafiya da matar alkalin take ciki.

Musa ya kai karar ne inda yake bukatar jaruma Gabon ta dawo masa da kudinsa,396,000 bayan da taki amincewa ta aure shi.

Tuni dai jarumar ta musalta cewa akwai wannan alƙawari a yayin zaman kotun da aka yi na farko a ranar 14 ga watan Yuni.

Jaridar Daily Trust ta rawaito cewa bayan da kowa ya gama hallara domin fara sauraren shari’ar na ranar Talata sai alkalin ya sanar cewa ya samun labarin an kai ɗaya daga cikin matansa a asibiti.

More News

Sabon gwamnan Taraba ya tsige kantomomin ƙananan hukumomi

Gwamnan jihar Taraba Agbu Kefas ya amince da rusa kwamitin riko na kananan hukumomi goma sha shida na jihar nan take. Rushewar wanda ke kunshe...

Abba Kabir ya kori shugaban hukumar jin dadin alhazan Kano

Kasa da sa’o’i 24 da hawan kujerar shugabancin jihar Kano, da sanyin safiyar Talatar nan ne Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya kori...

Yadda Buhari ya isa Daura bayan zamowa tsohon shugaban Najeriya

A yau Litinin ne shugaba Buhari ya isa mahaifarsa ta Daura bayan mika mulki ga Alhaji Asiwaju Bola Ahmed Tinubu. Tinubu dai ya zama shugaban...