Amina Amal Ta Kwanta Jinya Bayan Ta Sha Duka A Hannun Hadiza Gabon

Jaruma Amina Amal ta kwanta rashin lafiya bayan dukan da kawo wuka da fitacciyar Jaruma Hadiza Gabon ta yi ma ta tare da taimakon wasu karti maza.

Majiyar LEADERSHIP A YAU ta tabbatar da cewa, a yanzu haka yarinyar ta na fama da yanayi na rashin lafiya da kuma rudewa sakamakon mumman tashin hankalin da ta fuskanta tun a daren farko da Jaruma Gabon da tawagarta su ka far ma ta a gidanta da ke Kaduna.

Idan za a iya tunawa, Amal ta dora wani hotonta ne a Instagram wanda ke nuna cibiyarta a waje, lamarin da janyo zafafan martani daga masu yin sharhi a kan hoton, ciki har da wasu daga cikin ‘yan fim, kamar ita Gabon da Jaruma Aisha Tsamiya da
Darakta Hassan Giggs da sauransu.

To, amma abin mamaki shi ne Gabon ce kadai wacce Amal ta mayar wa da martani ta hanyar yin shagube kan dabi’a ta madigo, lamarin da ya fusata Gabon din.

Majiya mai tushe ta labarta wa wakilinmu cewa, sau uku ‘yan tawagar sun hada da maza kamar guda biyar ko shida, wadanda wasunsu a motar Hadiza Gabon din su ke yayin da wasu kuma su ke cikin babur din Adaidaita Sahu, cikinsu har da wasu fitattun ‘yan fim guda biyu; daya darakta ne ma.

More News

EFCC na neman Yahaya Bello ruwa a jallo

Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (Economic and Financial Crimes Commission) ta bayyana tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello a matsayin...

Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a...

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon Ɗaya Daga Cikin Ƴan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon ɗaya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...