A Najeriya musamman arewacin kasar, sabon abu ne a ga mace na buga wasan kwallon doki.
Amma Aisha Ahmad Suleiman, mai shekara 18 na neman yin fice a wasan kwallon doki.
Ta bayyana cewa ta fara da sha’awar dabbobi musamman dawakai wanda daga baya ta fara wasan kwallon doki.
Ta kuma ce ta fuskanci kalubale daban-daban bayan ta fara wasan kwallon dawaki.