Aisha Buhari Ta Gargadi Iyaye Su Hana ‘Ya’yansu Fada A Ranar Zabe

Madam Dolakpo Osinbajo ta bayyana hakan ne a wurin gangamin yakin neman zaben jami’iyyar APC da aka shiryawa mata da matasa a shiyyar jihohin tsakiyar Najeriya da aka gudanar a garin Lafia, babban birnin jahar Nasarawa.

Uwargidan mataimakin shugaban kasar wacce ta wakilci matar shugaban kasa, Hajiya A’isha Buhari ta zayyana ayyukan ci gaba da shugaba Muhammadu Buhari ya yiwa yara da mata da suka hada da shirin ciyar da ‘yan makarantar firamare kyauta wanda ya baiwa mata ayyukan yi, da tallafin kudi wa kananan ‘yan kasuwa da ake wa lakabi da Trader Moni da bayyana tabbacin kowa zai fita daga kangin talauci.

Da take magana da yawun uwargidan shugaban kasar A’isha Buhari, Dolakpo Osinbajo tace kada iyaye su kyale ‘ya’yansu su yi fada a lokacin zabe, sai dais u kada kuri’arsu su je gida su jira sakamakon zabe.

Ministan inganta wasanni da matasa yana cikin kusoshin jami’iyar APC da suka halarci taron, ya kuma ce gwamnatinsu ta yi rawar gani dalili kenan da suke bukata a sake zabenta. Yace an samu ci gaba a gyarar hanyoyi da tsaro da ma tattalin arzikin da saransu.

More News

EFCC na neman Yahaya Bello ruwa a jallo

Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (Economic and Financial Crimes Commission) ta bayyana tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello a matsayin...

Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a...

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon Ɗaya Daga Cikin Ƴan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon ɗaya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...