Aikin hajji: Miliyoyin musulmai na addu’o’i a dutsen Arfa |BBC

Mahajjata sun taru a Arfa a matsayin aiki mafi muhiimnaci na aikin hajji

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Aikin hajji da musulmai kan yi a kowace shekara ya kai matuka a yau, inda mutane kimanin miliyan biyu da rabi suka taru a dutsen Arfa inda za su wuni suna addu’o’i tare da karatun alkur’ani.

Mahajjatan sun taru a kan wannan dutse da filin da ke makwaftaka da shi ne a gab da fitowar rana.

Wannan wuri na Arfa na da nisan kimanin kilomita 15 daga birnin Makka.

A wannan dutse ne dai annabi Muhammad (S.A.W) ya gabatar da hudubarsa ta karshe, wadda ake kira hudubar ban-kwana.

Aikin Hajji na daga cikin ginshikan muslunci guda biyar, wanda ake so musulmi ya aikata akalla sau daya a tsawon rayuwarsa.

Mahajjata dai na fitowa ne daga dukakkanin fadin duniya, to amma Indonesia wadda ita ce ta fi kowace kasa yawan musulmai a duniya, ita ce ta fi kowace yawan musulmai a wurin na aikin hajji.

Hakkin mallakar hoto
AP

Daya daga cikin darussan da aikin hajji ke koyarwa shi ne karfafa dangantaka, da kuma nuna cewa kowane dan’adam daidai yake a gaban Allah madaukaki.

A lokacin aikin dukkanin mahajjata kan sanya sutura iri wadda ake kira ihrami.

More News

ÆŠalibai a Jami’ar Jos na zanga-zanga saboda rashin wuta da ruwa

Wasu daliban jami’ar Jos da ke jihar Filato a ranar Alhamis sun gudanar da zanga-zangar nuna rashin amincewarsu da matsalar karancin ruwa da rashin...

MTN yana ƙoƙarin ƙara kuɗin kati da data a Najeriya

Katafaren kamfanin sadarwa na MTN na kokarin kara kudin katin waya da na data a Najeriya. Kamfanin sadarwa mafi girma a nahiyar Afirka ya ba...

Gwamnatin Kano Ta Rage ₦500,000 A Kuɗin Aikin Hajjin Bana

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya sanar da yiwa maniyatan Aikin Hajji da suka fito daga jihar kyautar ₦500,000 domin su cika kuɗin...

Ƴan bindiga sun sace wani limami a jihar Kogi

Ƴan bindiga sun yi garkuwa da Quasim Musa babban limamin garin Iyara dake ƙaramar hukumar Ijumu ta jihar Kogi. Lamarin ya faru ne a ranar...