Aikin hajji: Miliyoyin musulmai na addu’o’i a dutsen Arfa |BBC

Mahajjata sun taru a Arfa a matsayin aiki mafi muhiimnaci na aikin hajji

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Aikin hajji da musulmai kan yi a kowace shekara ya kai matuka a yau, inda mutane kimanin miliyan biyu da rabi suka taru a dutsen Arfa inda za su wuni suna addu’o’i tare da karatun alkur’ani.

Mahajjatan sun taru a kan wannan dutse da filin da ke makwaftaka da shi ne a gab da fitowar rana.

Wannan wuri na Arfa na da nisan kimanin kilomita 15 daga birnin Makka.

A wannan dutse ne dai annabi Muhammad (S.A.W) ya gabatar da hudubarsa ta karshe, wadda ake kira hudubar ban-kwana.

Aikin Hajji na daga cikin ginshikan muslunci guda biyar, wanda ake so musulmi ya aikata akalla sau daya a tsawon rayuwarsa.

Mahajjata dai na fitowa ne daga dukakkanin fadin duniya, to amma Indonesia wadda ita ce ta fi kowace kasa yawan musulmai a duniya, ita ce ta fi kowace yawan musulmai a wurin na aikin hajji.

Hakkin mallakar hoto
AP

Daya daga cikin darussan da aikin hajji ke koyarwa shi ne karfafa dangantaka, da kuma nuna cewa kowane dan’adam daidai yake a gaban Allah madaukaki.

A lokacin aikin dukkanin mahajjata kan sanya sutura iri wadda ake kira ihrami.

More News

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon ĆŠaya Daga Cikin Ćłan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon É—aya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...

Gwamnatin Tarayya Za Ta Fara Rabon Gidaje 8925

Gwamnatin tarayya ta ce ta fara raba gidaje 8925  ga mutanen da suka nema kuma suka cancanci a basu a faɗin ƙasa baki ɗaya...

Ćłan Bindiga A Zamfara Sun Kashe Sakataren Jam’iyar PDP

Wasu ƴan bindiga da ba a san ko suwaye ba sun kashe, Musa Ille  sakataren jam'iyar PDP na ƙaramar hukumar Tsafe a jihar Zamfara. Zagazola...