Gwamnatin Kano ta kaddamar da wani kwamiti wanda zai fito da tsarin yadda za’a fara aiwatar da shirin samar da rugagen Fulani na zamani.
Gwamnan jihar Abdullahi Umar Ganduje ya shaidawa BBC cewa shirin samar da rugar a Kano ba iya Fulanin da ke jihar kawai ne za su amfana ba har da na sauran jahohin Najeriya.
Ya kuma ce shirin shi ne kawai da zai kawo karshen rikici tsakanin makiyaya da manoma.
Wannan na zuwa a yayin da ake ci gaba da musayar kalamai game da kiran Fulani su baro kudancin Najeriya da suke tafiya kiwo zuwa yankin arewaci.
Gwamna Ganduje ya ce dole a canza yadda ake gudanar da tsarin kiyo idan ana son magance matsalar rikicin makiyaya da manoma.
“Idan dai har ana son rigimar nan a daina ta dole a hana fulani tafiya da shanu daga arewa zuwa kudu,” in ji shi.
Ya kuma ce dole ya kasance a arewa an yi wuraren kiyo ga duk wanda zai yi kiyon shanu.
Gwamnan ya ce shirin ruga a Kano ya kunshi samar wa fulani hanyoyi na zamani ta hanyar ba ‘ya’yansu ilimi da asibiti da kuma banki na Islama da samar da kiyo na zamani da kuma yadda shanu za su samu abinci domin samar da wadataccen nono.
Gwamnatin Kano dai ta dage kan kaddamar da shirin duk da gwamnatin tarayya ta dakatar da kudirinta na samar da rugagen, saboda yadda kudirin ya janyo ce-ce-ku-ce.