A ranar Alhamis, 4 ga watan Afrilu, 2019 ake sa ran kotun da ke sauraran kararrakin zabe, reshen jihar Kano za ta fara zamanta domin saurarar karar da jam’iyar PDP ta shigar game da zaben cike gibin da aka gudanar a ranar Asabar 23 ga watan Maris. Rahotanni sun bayyana cewar kotun za ta kaddamar da zaman nata na farko da misalin karfe 10 na safiya.