[ad_1]
Mutane 12 ake fargabar sun mutu lokacin da wasu yan fashi da makami suka kai hari ofishin ƴansanda da kuma wasu bankunan kasuwanci biyu a jiya Talata dake Igarra, hedkwatar ƙaramar hukumar Akoko-Edo ta jihar Edo.
Bankunan da abin ya shafa sune Bankin Unity da kuma Keystone.
Cikin mutane 12 da aka kashe a harin akwai É—ansanda, É—aurarru biyu da kuma wasu kwastomomin bankin.
An gano cewa yan fashin sai da suka fara kai hari ofishin Ć´ansanda dake kusa da bankin a wani abu da ake gani sun yi ne domin hana Ć´ansandan mayar da martani yayin da suke aikata fashin.
Ƴanfashin sun kuma kona sabuwar motar aiki ta sabon baturen ƴansanda na shiya da aka tura yankin suka kuma kashe d’ansanda daya da kuma wasu dake daure a ofishin.
ĆŠaurarru an an kama sune da safe kan rashin cikakkun takardun abin hawa.
An gano cewa yan fashin sun gaza samun nasarar shiga ma’ajiyar kudin bankunan inda suka shiga harbin mutanen dake harabar.
Mai magana da yawun rundunar Ć´ansandan jihar, Chidi Nwabuzor ya tabbatar da faruwar lamarin.
[ad_2]