Ƴanbindiga sun kashe shugaban jam’iyar APC a jihar Imo

Yan bindiga sun harbe, Mista Ifeanyi Ozoemena,shugaban jam’iyar APC na mazabar Logara/Umuohiagu dake karamar hukumar Ngor Okpala ta jihar Imo.

Wakilin jaridar Daily ya tattara bayanan dake cewa an harbe Ozoemena har lahira ranar Talata da daddare sa’o’i biyu bayan da ya jagoranci taron jam’iyyarsa a mazabarsa a shirye shiryen da suke na tunkarar zaben shugaban dana yan majalisun tarayya.

A cewar wadanda suka sheda abinda ya faru, an harbe shugaban na APC a cikin gidansa lokacin da iyalansa ke tare da shi.

Mataimakin shugaban kungiyar cigaban al’ummr Logara wanda ya tabbatar da faruwar kisan kan da ya bayyana da abu marar dadin ji.

Kwamishinan ƴansandan jihar, Dasuki Galadanchi ya tabbatar da faruwar lamarin a tattaunawar da ya yi da wakilin jaridar Daily Trust ta wayar tarho inda ya ce tuni jami’an tsaro suka dauke gawar.

More News

EFCC na neman Yahaya Bello ruwa a jallo

Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (Economic and Financial Crimes Commission) ta bayyana tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello a matsayin...

Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a...

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon Ɗaya Daga Cikin Ƴan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon ɗaya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...