Ƴanbindiga sun kashe shugaban jam’iyar APC a jihar Imo

Yan bindiga sun harbe, Mista Ifeanyi Ozoemena,shugaban jam’iyar APC na mazabar Logara/Umuohiagu dake karamar hukumar Ngor Okpala ta jihar Imo.

Wakilin jaridar Daily ya tattara bayanan dake cewa an harbe Ozoemena har lahira ranar Talata da daddare sa’o’i biyu bayan da ya jagoranci taron jam’iyyarsa a mazabarsa a shirye shiryen da suke na tunkarar zaben shugaban dana yan majalisun tarayya.

A cewar wadanda suka sheda abinda ya faru, an harbe shugaban na APC a cikin gidansa lokacin da iyalansa ke tare da shi.

Mataimakin shugaban kungiyar cigaban al’ummr Logara wanda ya tabbatar da faruwar kisan kan da ya bayyana da abu marar dadin ji.

Kwamishinan ƴansandan jihar, Dasuki Galadanchi ya tabbatar da faruwar lamarin a tattaunawar da ya yi da wakilin jaridar Daily Trust ta wayar tarho inda ya ce tuni jami’an tsaro suka dauke gawar.

More News

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaƙi da yiwa tattalin arzikin ƙasa ne ya hana shi bayyana...

Ƴan sanda sun kama mutane biyu dake samarwa ƴan fashin daji makamai a jihar Kaduna

Rundunar ƴan sandan jihar Kaduna ta ce tana tsare da wasu mutane biyu da ake zargi da safarar bindiga a jihar. A wata sanarwa ranar...

An kori sojojin Najeriya biyu saboda satar kebul a matatar Dangote

Rundunar sojin Najeriya ta tabbatar da korar wasu sojoji biyu da ake zargi da satar igiyoyin sulke a harabar matatar Dangote da ke jihar...

Magoya bayan APC da dama sun koma NNPP a Kano

Jam'iyar NNPP ta karɓi magoya bayan jam'iyar APC da dama a jihar Kano. Mataimakin gwamnan jihar Kano, Aminu Abdul Salam Gwarzo shi ne ya karɓi...