Ƴan Sanda A Kano Sun Samu Nasarar Harbe Wani Dan Fashi Da makami

[ad_1]








Lamarin ya faru ne a yau Laraba da misalin karfe uku da rabi a sabuwar Unguwar Railway inda ‘yan daban suka addabi mutanen jihar Kano da fashi da makami.

Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Kano SP Majia ya ce jami’an nasu sun yi arrangama da dan daban kuma aka yi nasarar bindige shi bayan sun sassari dan sanda daya a kai, hannu da sassan jikinsa, wanda yake sanye da riga ‘yar shara a jikin sa.

SP MAJIA ya kara da cewa wasu daga cikin wadannan ‘yan daba ko ‘yan fashi da makami da suka gudu sun bar mugayen makaman da suke amfani da su wajen aikata miyagun laifuka bayan arangama da ‘yan sandan kuma jikin gawar dan fashin an sami katin zabe (Voters Card) guda 2 da sunaye daban-daban.

Daga karshe ya bayanna cewa Kwamishinan ‘Yan sanda CP Rabiu Yusuf ya yi jinjina ga DPO na shiyyar Nassarawa CSP Abubakar Argungu da jami’ansa kan samun wannan nasara.




[ad_2]

More News

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miƙata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaƙi da yiwa tattalin arzikin ƙasa ne ya hana shi bayyana...

Ƴan sanda sun kama mutane biyu dake samarwa ƴan fashin daji makamai a jihar Kaduna

Rundunar ƴan sandan jihar Kaduna ta ce tana tsare da wasu mutane biyu da ake zargi da safarar bindiga a jihar. A wata sanarwa ranar...