Ƴan Sanda A Kano Sun Samu Nasarar Harbe Wani Dan Fashi Da makami

[ad_1]








Lamarin ya faru ne a yau Laraba da misalin karfe uku da rabi a sabuwar Unguwar Railway inda ‘yan daban suka addabi mutanen jihar Kano da fashi da makami.

Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Kano SP Majia ya ce jami’an nasu sun yi arrangama da dan daban kuma aka yi nasarar bindige shi bayan sun sassari dan sanda daya a kai, hannu da sassan jikinsa, wanda yake sanye da riga ‘yar shara a jikin sa.

SP MAJIA ya kara da cewa wasu daga cikin wadannan ‘yan daba ko ‘yan fashi da makami da suka gudu sun bar mugayen makaman da suke amfani da su wajen aikata miyagun laifuka bayan arangama da ‘yan sandan kuma jikin gawar dan fashin an sami katin zabe (Voters Card) guda 2 da sunaye daban-daban.

Daga karshe ya bayanna cewa Kwamishinan ‘Yan sanda CP Rabiu Yusuf ya yi jinjina ga DPO na shiyyar Nassarawa CSP Abubakar Argungu da jami’ansa kan samun wannan nasara.




[ad_2]

More News

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaƙi da yiwa tattalin arzikin ƙasa ne ya hana shi bayyana...

Ƴan sanda sun kama mutane biyu dake samarwa ƴan fashin daji makamai a jihar Kaduna

Rundunar ƴan sandan jihar Kaduna ta ce tana tsare da wasu mutane biyu da ake zargi da safarar bindiga a jihar. A wata sanarwa ranar...

An kori sojojin Najeriya biyu saboda satar kebul a matatar Dangote

Rundunar sojin Najeriya ta tabbatar da korar wasu sojoji biyu da ake zargi da satar igiyoyin sulke a harabar matatar Dangote da ke jihar...

Magoya bayan APC da dama sun koma NNPP a Kano

Jam'iyar NNPP ta karɓi magoya bayan jam'iyar APC da dama a jihar Kano. Mataimakin gwamnan jihar Kano, Aminu Abdul Salam Gwarzo shi ne ya karɓi...